Dollar

38,2552

0.34 %

Euro

43,8333

0.15 %

Gram Gold

4.076,2000

0.31 %

Quarter Gold

6.772,5700

0.78 %

Silver

39,9100

0.36 %

Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta tabbatar da mutuwar mutum 17 a wasu hare-hare biyu da ake zargin makiyaya sun kai kan al'ummomin manoma a jihar ta Benue.

'Yan sanda a Nijeriya sun tabbatar da mutuwar mutum 17 a Benue

Aƙalla mutum 17 sun rasu bayan wasu da ake zargin makiyaya ne sun kai hari kan wasu al’ummomi a Jihar Benue, kamar yadda rundunar ‘yan sandan ƙasar ta tabbatar.

Lamarin ya faru ne dai a Gbagir da ke Ƙaramar Hukumar Ukum da kuma a Ƙaramar Hukumar Logo duka da ke yankin Sankera a Jihar Benue.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun ƙarin rikici tsakanin manoma da makiyaya a wasu sassan ƙasar.

A sanarwar da mai magana da yawun ‘yan sanda reshen Benue Sewuese Anene ta fitar a ranar Juma’a, ta ce ‘yan bindigan sun fara kashe mutum biyar a harin da suka kai Gbagir, inda daga baya kuma wasu ‘yan bindigan kuma suka kashe wasu mutum 12 a Logo.

‘Yan sandan sun yi watsi da rahotannin shafukan sada zumunta da ke cewa an kashe fiye da mutum 100 a harin.

Harin na baya-bayan nan ya faru ne kwana biyu bayan kashe mutum 11 a Otukpo da ke Jihar Benue, haka kuma ƙasa da mako guda bayan an kashe fiye da mutum 50 a Jihar Filato da ke makwabtaka.

Tun daga shekarar 2019, wannan rikicin ya yi sanadin mutuwar rasa rayukan fiye da mutum 500 a yankin da kuma tilasta wa mutum miliyan 2.2 barin gidajensu, kamar yadda wani kamfani da ke bincike na SBM Intelligence ya bayyana.

 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#