Sport
Dollar
37,9330
-0.04 %Euro
41,2125
0.42 %Gram Gold
3.808,1600
0.23 %Quarter Gold
6.332,2600
1.97 %Silver
41,2000
-1.11 %Ƙage da zargin ƙarya na cewa ana ƙyamar Yahudawa na baya bayan nan shi ne wanda aka yi wa sanannen Farfesa Cemal Kafadar, wanda aka cire daga shugabancin Cibiyar Nazarin Gabas ta Tsakiya ta Jami’ar Harvard.
Daraktan Sashen Watsa Labarai na Turkiyya ya yi Allah wadai da ƙoƙarin da ƙungiyoyin masu goyon bayan Isra'ila ke yi na rufe bakin muryoyin da ke goyon bayan Falasdinu ta hanyar yi musu ƙagen cewa suna nuna ƙiyayya ga Yahudawa.
“Wannan aiki ya kai ga wasu daga cikin manyan cibiyoyin ilimi a Amurka, kamar Harvard,” in ji Altun a cikin wata sanarwa a ranar Asabar, yana nuni da cire Farfesa Cemal Kafadar, Ba’amurke ɗan asalin Turkiyya daga shugabancin Cibiyar Nazarin Gabas ta Tsakiya ta Harvard.
Ya ƙara da cewa wannan mataki, wanda aka ɗora bisa “zarge-zargen ƙarya da nuna ƙiyayya ga Yahudawa,” yana nuna rashin daidaito na jami’o’in Amurka waɗanda tsawon lokaci suke ikirarin ba da fifiko na ɗabi’a kan 'yancin ilimi da 'yancin faɗin albarkacin baki.
Cire wannan fitaccen masanin tarihin Usmaniyya, Kafadar, ya zo ne kwanaki kaɗan bayan wata ɗaliba mai karatun digiri na uku 'yar asalin Turkiyya a Amurka, Rumeysa Ozturk, ta shiga hannun hukuma kuma aka yi ƙoƙarin korarta, bisa rahotanni cewa wani shiri na Canary Mission — wani shafin intanet mai goyon bayan Isra'ila da ke sanya sunayen ɗalibai da masu fafutukar goyon bayan Falasdinu a jerin sunayen da ake zargi — ya yi tasiri.
“Matsin lambar gwamnatin Amurka kan jami’o’i, da kuma cire mutane daga Amurka saboda ra’ayinsu da fafutukarsu don Falasdinu, ya saba wa ƙa’idojin mutuntaka da Amurka ta daɗe tana karewa,” in ji Altun, yana zargin abokan Isra'ila na Yamma da yin wani “bi-ta-da-ƙulli.”
Ya yi kira ga cibiyoyin ilimi na Yamma da su “tsaya tsayin daka kan buƙatun da ba su dace ba da kuma masu tsanani na kai hari ga ɗalibai da masana na ƙasashen waje,” yana mai jaddada cewa irin waɗannan ƙungiyoyin Zionist (masu tsananin aƙidar son kafa ƙasar Isra’ila) “sun koma amfani da dabaru marasa kyau don hana sahihiyar suka da kuma fafutuka a cikin lumana.”
Daraktan sashen watsa labaran ya sake tabbatar da cewa Turkiyya tana ƙin duk wani yunƙuri na nuna fafutukar goyon bayan Falasdinu a matsayin ƙiyayya ga Yahudawa.
Comments
No comments Yet
Comment