Sport
Dollar
37,9310
-0.05 %Euro
41,2266
0.41 %Gram Gold
3.809,9500
0.27 %Quarter Gold
6.332,2600
1.97 %Silver
41,2200
-1.05 %"Ba za mu ƙyale waɗanda suke ƙoƙarin yi wa kan iyakokin Syria zagon ƙasa tare da dawwamar da rashin zaman lafiya a kan iyakokinmu na kudu ba," in ji Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan.
Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya ce Turkiyya ba za ta lamunci ƙeta haƙƙin kan iyakokin ƙasar Syria tare da dawwamar da rikici a kan iyakar kudancin ƙasar ba.
A wani jawabin ƙaramar Sallah da ya yi ranar Lahadi – ƙarshen azumin watan Ramadan --Erdogan ya bayyana cewa Turkiyya za ta “ci gaba da aikin da muka fara bisa manufarmu ta ‘Turkiyya ba tare da ta’addanci ba’ kuma daidai da tsare-tsarenmu.”
Ya yi gargaɗin cewa Ankara ba ta da “haƙuri mara iyaka” kan batun kuma yana sa ran ƙungiyoyin ta’addancin PKK/YPG su watse da kansu tare da “ajiye makamansu gabaɗaya ba tare da ɓata lokaci ba.”
A cikin kusan shekara 40 da ta shafe tana kai hare-haren ta’addanci kan Turkiyya, ƙungiyar PKK – wadda Turkiyya da Amurka da kuma Ƙungiyar Tarayyar Turai suka ayyana a matsayin ƙungiyar ta’addanci – ta yi sanadin mutuwar sama da mutum 40,000 ciki har da mata da yara da jarirai.
Ƙungiyar YPG/PYD, wadda ke kuma amfani da suna SDF, ita ce reshen PKK a Syria.
‘Yan ta’addan PKK suna yawan ɓuya a arewacin Iraƙi domin kitsa hare-hare a Turkiyya yayin da YPG/PYD ta yi ƙoƙarin kafa wata hanyar ta’addanci a arewacin Syria kusa da kan iyakar Turkiyya.
Comments
No comments Yet
Comment