Dollar

38,1588

0.3 %

Euro

43,6101

1.61 %

Gram Gold

3.958,7400

2.25 %

Quarter Gold

6.529,2600

2.67 %

Silver

39,4700

3.6 %

Kwanan nan ne dai cacar baka ta kaure tsakanin Mali da Aljeriya kan zargin da Mali ta yi na cewa Aljeriya ta kakkaɓo jirgi mara matuƙinta.

Cacar-bakin da Mali da Aljeriya ke yi abin damuwa ne — ECOWAS

Ƙungiyar Raya Tattalin Aziƙin Yammacin Afirka (ECOWAS) ta bayyana damuwa dangane da yadda dangantaka tsakanin ƙasashen Mali da Aljeriya ta yi tsami.

A wata sanarwar da ta fitar ranar Laraba a shafinta na X, hukumar ta ECOWAS ta ce cikin damuwa ne take bibiyar cacar-bakan da ake yi tsakanin ƙasar Mali da Aljeriya ta saƙonnin sanarwar da suke fitarwa cikin ‘yan kwanakin nan.

“A madadin ƙasashe mambobin ƙungiyar ECOWAS, hukumar ta bayyana damuwarta matuƙa game da yanayin,” in ji ECOWAS.

 “Tana kira ga Mali da Aljeriya su rage tashin hankali su rungumi tattaunawa tare da amfani da tsare-tsaren yanki da na nahiya domin warware matsalolinsu,” in ji sanarwar.

Kwanan nan ne dai cacar-baka ta kaure tsakanin Mali da Aljeriya kan zargin da Mali ta yi na cewa Aljeriya ta kakkaɓo jirgi mara matuƙinta.

Aljeriya ta rufe sararin samaniyarta ga Mali bisa abin da ta kira “keta doka a-kai-a-kai” bayan ƙasashen Mali da Burkina Faso da Nijar sun yi wa jakadunsu kiranye daga Aljeriya bayan da aka kakkaɓo jirgin sama mara matuƙin Mali ɗin.

 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#